Classic TV

Classic TV

Share

Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Classic TV, Abuja.

kuci gaba da Bibiyar Classic Tv Domin samun ingantattaun Labaru

Domin Tallata Hajarku Kasuwanci, Siyasa, Harkokin Yauda Kullum
Tuntibemu ta wannann Layuka

08066678656
08022975656

Photos from Classic TV's post 23/06/2026

Gasar kofin duniya: Lamine Yamal ya faɗi cikin sujjada nan take bayan ya zura ƙwallo a ragar Saudiyya

Photos from Classic TV's post 23/06/2026

WATA SABUWA: Za mu maka Kwankwaso a kotu bisa siye fom din yan takarar PRP na Kano su 69 - Masu ruwa da tsaki

Masu Ruwa da Tsaki na Jam’iyyar PRP na shiyyar Arewa maso Yamma sun zargi Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da saye fama-faman yan takarar jam'iyyar na Kano, lamarin da s**a ce zai iya hana mambobin da s**a cancanta damar tsayawa takara.

Shugaban kungiyar masu ruwa da tsakin, Abdulkadir Musa Guza ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Kano a yau Lahadi.

Ya ce jam'iyyar na zargin Kwankwaso da saye fom ɗin takara na dukkan matakai 69 na jam’iyyar PRP, inda ya zargi tsohon gwamnan da zagon kasa bayan shi ba dan jam'iyyar ba ne.

Guza ya bayyana damuwa ga makomar dimokuraɗiyya da tsarin gudanar da harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa.

A cewarsa, matakin zai iya hana mambobin jam’iyyar da s**a cancanta kuma suke da niyyar tsayawa takara damar samun tikitin jam’iyyarsu.

Ya bayyana lamarin a matsayin “fashin siyasa” wanda zai iya haifar da rikice-rikice da ruɗani a harkokin zaɓe idan ba a dakatar da shi ba.

Guza ya jaddada cewa PRP jam’iyya ce mai bin ƙa’idojin dimokuraɗiyya kuma ba za ta amince da duk wani yunƙuri na kwace ikon tafiyar da harkokinta ba.

Ya yi kira ga Kwankwaso da ya bar jam’iyyun siyasa su gudanar da harkokinsu cikin ‘yanci da adalci, yana mai cewa bai k**ata a tsoma baki cikin harkokin PRP ba.

Shugaban dandalin ya kuma yi gargaɗin cewa idan aka ci gaba da abin da ya kira katsalandan a harkokin jam’iyyar, za su nemi mafita ta hanyar kotu domin kare haƙƙin mambobinsu da martabar jam’iyyar.

23/06/2026

Kotu ta bada umarnin tsare Sowore a gidan gyaran hali na Kuje

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa ranar 24 ga Yuni, 2026.

Ana tuhumar Sowore da laifuka biyu da s**a shafi amfani da yanar gizo wajen cin mutunci da kuma bibiyar wani ta hanyar sadarwa, bayan ya bayyana Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin “mai laifi” a wasu saƙonnin da ya wallafa a kafafen sada zumunta a watan Agustan 2025.

Kotun ta ce Sowore ya ci gaba da faɗin kalamansa duk da buƙatar da jami’an DSS s**a yi masa na goge saƙonnin, yana mai cewa yana amfani da ‘yancin faɗin albarkacin baki ne.

Tun da farko, alkalin kotun, Mai Shari’a Mohammed Umar, ya yi watsi da buƙatar da Sowore ya gabatar na soke tuhumar, yana mai cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjojin da s**a isa a ci gaba da sauraron shari’ar.

Bayan lauyoyinsa sun janye daga shari’ar a watan Yuni, Sowore ya zaɓi kare kansa da kansa tare da zargin alkalin da nuna son kai. Sai dai a ranar Litinin kotun ta yi watsi da ƙorafinsa, tare da umartar a tsare shi a Kuje.

Gwamnati na zargin cewa kalaman da Sowore ya wallafa a intanet sun kasance na ƙarya kuma an yi su ne domin tayar da hankalin jama’a, amma shi ya musanta zargin tare da bayyana kansa a matsayin mara laifi. Ana sa ran za a ci gaba da sauraron shari’ar a tsakiyar makon nan.

23/06/2026

Obasanjo Akan Gaɓar Barin Duniya! ku karanta wannan rubutun

Shin Obasanjo Ya Shirya Mutuwa?

Olusegun Obasanjo mai shekaru 94 ya rubuta wasiƙa mai taɓa zuciya ga ’yan Najeriya. Shin hakan na nufin yana shirin barin duniya? Ga abin da ya rubuta:

’Yan uwana ’yan ƙasa,

Mutane suna cewa rayuwa tana da tsawo. Suna cewa, “Ka rayu a hankali, lokaci yana da yawa.” Amma ni ina da shekaru 94 yanzu, kuma zan iya cewa da tabbaci cewa hakan ba gaskiya ba ne. Rayuwa ba ta da tsawo; tana wucewa k**ar ƙiftawar ido. Yayin da nake gab da barin wannan duniya, zuciyata na son in bar muku wasu darussa.

Na tara dukiya, na samu girma da suna, amma yau duk waɗannan suna k**a da ƙura a kusurwar ɗakina. Idan na miƙa hannu yanzu, babu ɗaya daga cikinsu da zai bi ni.

Darasi na Farko: Kada Ka Rayu Cikin Jira

Babban ɓangaren rayuwata ya shuɗe cikin jira.

A makaranta, na yi tunanin rayuwa za ta fara ne bayan na sami takardar shaidar kammala karatu.

Da na samu aiki a soja, sai na riƙa jiran ƙarshen mako.

Da na yi aure, sai na riƙa jiran yarana su girma.

Da s**a girma, sai na fara jiran ritaya.

Na ɗauki kowace rana a matsayin wata mataki ce kawai, ina tunanin ainihin rayuwa tana gaba. Amma yanzu na gane cewa babu wata manufa ta ƙarshe; tafiyar kanta ita ce rayuwa.

Darasi na Biyu: Zinariya Ba Abinci Ba Ce

Na kwashe shekaru 50 ina tara dukiya. Na yi aiki tuƙuru har na rasa lokuta masu muhimmanci tare da iyalina.

Na sayi manyan gidaje, motoci masu tsada da kayan alatu, amma yanzu da nake gab da tafiya, na gane cewa babu ɗaya daga cikin waɗannan da zai bi ni.

Har yanzu ina tuna ranar da ɗiyata ta kira ni zuwa lambu domin in ga wata ƙaramar ƙwari da ta gano. Na ce mata, “Ba yanzu ba, ina aiki.” Yau har yanzu ina jin zafin wannan lokacin da na rasa.

Darasi na Uku: Rushe Katangar Da Ke Zuciyarka

A lokacin ƙuruciyata, na yi tunanin nuna tausayi ko neman afuwa alama ce ta rauni.

Ina da wani ɗan’uwa da muka taso tare. Wata rana muka yi saɓani kan wani ƙaramin abu. Ban tuna ma abin da ya jawo ba yanzu.

Na jira shi ya fara neman sulhu. Shekaru s**a shuɗe. Wata rana aka kira ni aka ce ya mutu.

A lokacin ne na gane cewa na yi daidai, amma na rasa ɗan’uwana.

Idan kana son wani, ka gaya masa yau. Idan ka yi kuskure, ka nemi afuwa yau. Gobe ba ta da tabbas.

Darasi na Hudu: Tsoro Inuwa Ce Kawai

Ina da shekaru 22 lokacin da nake son zama marubuci. Ina da littafin rubutu cike da mafarkai da labarai.

Amma ban taɓa rubuta littafin ba saboda tsoron a yi min dariya ko in gaza.

Yanzu hannuwana suna rawa, idanuna sun yi rauni. Wannan littafin har yanzu yana cikina.

Babban abin takaici a rayuwa ba mutuwa ba ce; mafarkan da muka kashe tun muna raye ne.

Kada ka ci gaba da jinkirta abin da zuciyarka ke so. Ka fara yau. Ko da ka faɗi, aƙalla za ka ce, “Na yi ƙoƙari.”

Kammalawa

Agogona na ƙara yin ƙara a kunnena yanzu. Na ajiye damuwa, girman kai da tsoro.

Kai har yanzu kana raye. Kana da wata rana.

Kada ka ɓata ta.

Ka kalli hannuwanka. Ka motsa yatsunka. Ka ji numfashinka.

Duk wannan ni’ima ce.

Kada ka jira ka kai shekaru 94 kafin ka gane yadda rayuwa take da kyau.

Ka rayu yanzu.

Sai an jima.

Takaitawa

Rayuwa gajera ce kam.

22/06/2026

Anya Izuwa Yanzu ana iya samun masu Sana'ar Going ( Achaba ) suyi full tank k**ar yanda ake yi shekarun baya ?

22/06/2026

Meyasa Kuria Ɗaya take da Mahimmanci a zabe
Daure ka kallah

Temakemu da Follow likes and comments 🙏🙏

21/06/2026

JAMA'ARE EMIRATE COUNCIL.BAUCHI STATE...FOUNDED BY HARDO SALE 1803.

20/06/2026

ZAƁEN GWANI 2026

Yanzu lokaci ne na zaɓar wanda zai wakilce mu a Majalisar Jiha. Ka zaɓi ɗan takarar da kake ganin ya fi dacewa, sannan ka bayyana dalilan da s**a sa kake son ya wakilce ka.

1. Hon Aminu Isah Yuguda (ADC)
2. Hon Lukman Adamu (ZLP)
3. Hon Mubarak Haruna ( APC)
4. Hon Sani Bello Hanafari. (APM)
5. Hon Muhammad Sale Malallan (PRP)
6. Hon Abdulmunin Mohammed Halliru (PDP)

✅ Shin yana da nagarta da gaskiya?

✅ Shin yana da ƙwarewa da hangen nesa?

✅ Shin yana kusa da al'umma kuma yana sauraron matsalolinsu?

✅ Shin yana da tarihin kawo ci gaba da taimakon jama'a?

Ra'ayoyinku suna da matuƙar muhimmanci, domin za su taimaka wa masu zaɓe wajen fahimtar cancantar 'yan takara da kuma yanke shawara mai kyau.

Ka faɗi sunan wanda ka zaɓa tare da dalilanka a sashen sharhi.

"Kuri'arka, muryarka ce; ka yi amfani da ita wajen zaɓar wanda zai kawo ci gaba ga al'ummarka."

20/06/2026

📢 SANARWA GA MASU BI BIYAR SHAFINMU

Da ƙarfe 8:00 na dare yau, za mu gudanar da Online Vote na masu neman kujerar Majalisar Jiha ta Jama'are, In Sha Allah.

Muna gayyatar ku da ku fito ku bayyana ra'ayoyinku cikin mutunci da adalci.

Wanda za ka zaɓa ya cancanta? ❓
Me ya sa za ka zaɓe shi? ❓
Wadanne kyawawan halaye ko ayyuka ka gani a tare da shi? ❓
Me kake ganin zai kawo wa al'ummar Jama'are idan ya samu nasara?

Ra'ayoyinku za su taimaka wajen fahimtar abin da jama'a ke so da kuma abin da suke tsammani daga shugabanninsu.

🗳️ Ku kasance tare da mu da ƙarfe 8:00 na dare domin kaɗa ƙuri'arku da bayyana hujjojin zaɓinku.

Allah Ya ba mu shugabanci nagari, Ya kuma zaɓa mana mafi alheri. 🤲🏻
fans

19/06/2026

WAKUKE FATA YAKASANCE CHAIRMAN A JAMA'ARE LOCAL GOVT AZABE MAIZUWA AUGUST 2027 ACIKIN JERIN WADANNAN MUTANE:-

1. Hon Inuwa Moisha
2. Hon Bello Mahmood.
3. Hon Saleh Malle
4. Hon shehu Wadaji
5. Hon Saleh Sabonkafi
6. Rtd permsec Abubakar Mansur
7. Hon Samaila Yusuf Jarma
8. Comr Usman Idrees Ba'indeeye

Zaka iya saka Wanda kake fata

Want your school to be the top-listed School/college in Abuja?

Click here to claim your Sponsored Listing.

Location

Telephone

Address


Abuja